ABNA24 : Jaridar Premium times ta Najeriya ta bayyana cewa tun ranar 6 ga watan Afrilun da muke ciki ne hukumar ta EFCC ta mikawa tsohon gwamnan wasikar gayyata zuwa ofishinta da ke birnin Sokoto a ranar 8 ga watan Afrilun da muke ciki, amma Yari bai amsa gayyatar ba sai a jiya Talata 20 ga wata.
Labarin ya kara da cewa tsohon gwamnan ya isa ofishin hukumar ne da misalin karfe 11 na safe kuma har zuwa karfe 7 na yamma ya na tare da jami’an hukumar. Har’ila yau na ce ya zuwa lokacin hada wannan rahoton an bada belinsa amma bai cika sharuddan karban belin ba.
A cikin watan Fabrairu da ya gabata ma, tsohon gwamnanan ya sha tambayoyi a ofishin hukumar ta EFCC da ke birnin Lagos kan kokarin yin sama da fadi da wasu kudade kimani naira biliyon 300 da ke cikin wani asusu a bankin Generation Bank a birnin na Lagos.
342/